Home
Categories
EXPLORE
True Crime
Comedy
Society & Culture
Business
History
Sports
Technology
About Us
Contact Us
Copyright
© 2024 PodJoint
00:00 / 00:00
Sign in

or

Don't have an account?
Sign up
Forgot password
https://is1-ssl.mzstatic.com/image/thumb/Podcasts221/v4/b6/6f/72/b66f7251-c078-a8f3-29b4-32bed8298330/mza_9500036076761979941.jpg/600x600bb.jpg
Najeriya a Yau
Muslim Muhammad Yusuf, Ummu Salmah Ibrahim
907 episodes
1 day ago
Send us a text A fagen siyasar Najeriya a halin yanzu, ana ta ce-ce-ku-ce kan wacce ce babbar jam’iyyar adawa da za ta iya tsayawa ƙafada da ƙafada da jam’iyyar APC mai mulki. Wannan takaddama ta fi karkata ne tsakanin jam’iyyar PDP, wacce ta dade tana taka rawa a matsayin babbar jam’iyyar adawa bayan ficewarta daga mulki a 2015, da kuma jam’iyyar ADC, wacce a ‘yan shekarun nan ta fara samun karɓuwa sakamakon shigar wasu manyan ‘yan siyasa da kuma ƙoƙarin gina sabuwar haɗaka a matsayin madadi...
Show more...
News Commentary
News,
Politics
RSS
All content for Najeriya a Yau is the property of Muslim Muhammad Yusuf, Ummu Salmah Ibrahim and is served directly from their servers with no modification, redirects, or rehosting. The podcast is not affiliated with or endorsed by Podjoint in any way.
Send us a text A fagen siyasar Najeriya a halin yanzu, ana ta ce-ce-ku-ce kan wacce ce babbar jam’iyyar adawa da za ta iya tsayawa ƙafada da ƙafada da jam’iyyar APC mai mulki. Wannan takaddama ta fi karkata ne tsakanin jam’iyyar PDP, wacce ta dade tana taka rawa a matsayin babbar jam’iyyar adawa bayan ficewarta daga mulki a 2015, da kuma jam’iyyar ADC, wacce a ‘yan shekarun nan ta fara samun karɓuwa sakamakon shigar wasu manyan ‘yan siyasa da kuma ƙoƙarin gina sabuwar haɗaka a matsayin madadi...
Show more...
News Commentary
News,
Politics
Episodes (20/907)
Najeriya a Yau
Sharuddan Da Jam'iyya Za Ta Cika Kafin Kiran Ta Babban Jam'iyyar Adawa
Send us a text A fagen siyasar Najeriya a halin yanzu, ana ta ce-ce-ku-ce kan wacce ce babbar jam’iyyar adawa da za ta iya tsayawa ƙafada da ƙafada da jam’iyyar APC mai mulki. Wannan takaddama ta fi karkata ne tsakanin jam’iyyar PDP, wacce ta dade tana taka rawa a matsayin babbar jam’iyyar adawa bayan ficewarta daga mulki a 2015, da kuma jam’iyyar ADC, wacce a ‘yan shekarun nan ta fara samun karɓuwa sakamakon shigar wasu manyan ‘yan siyasa da kuma ƙoƙarin gina sabuwar haɗaka a matsayin madadi...
Show more...
4 days ago
23 minutes

Najeriya a Yau
Yadda Ya Kamata Ku Gudanar Da Rayuwa A Shekarar 2026
Send us a text Shekarar 2026 ta zo a wani lokaci da ’yan Najeriya da dama ke fuskantar matsin tattalin arziki, da sauye-sauyen siyasa, da kuma ƙalubalen rayuwa da ke bukatar sabon tunani. Wannan ba lokaci ba ne na fatan samun sa’a kawai, lokaci ne na tsara hanya, da ɗaukar matakai, da yin gyara a rayuwar yau da kullum. A wannan shiri, za mu duba yadda ya kamata ’yan Najeriya su fara sabuwar shekara ta 2026 ta hanyoyi masu ma’ana—daga kula da yadda zasu sarrafa kuɗi da sana’a, zuwa kiwon lafiy...
Show more...
5 days ago
17 minutes

Najeriya a Yau
Siyasa Da Tsare-tsaren Gwamnati Da Suka Dabaibaye 2025
Send us a text Yayin da muke bankwana da shekarar 2025, siyasar Najeriya ta kasance cike da sauye-sauye, rikice-rikice, da kuma manyan al’amura da suka shafi iko, jam’iyyu da shugabanci. Shekarar ta shaida sauyin sheƙa na ‘yan siyasa, rikicin cikin gida a wasu jam’iyyu, da kuma fafutukar karɓar ragamar mulki a jihohi da matakin tarayya, lamarin da ya ƙara zafafa siyasar ƙasa. A bangaren tsare-tsaren gwamnati kuwa, 2025 ta kasance shekara mai ɗauke da tsauraran manufofi da suka shafi tattalin ...
Show more...
1 week ago
21 minutes

Najeriya a Yau
Waiwaye Kan Manyan Kalubalen Tsaro Da Suka Faru A 2025
Send us a text A shekarar 2025, Najeriya ta fuskanci manyan ƙalubalen tsaro da suka fi daukar hankali, musamman hare-haren ‘yan bindiga, garkuwa da mutane, da ta’addanci a jihohin Arewa kamar Zamfara, da Katsina da Sokoto da Kaduna da kuma Borno. Hare-haren sun yi sanadin rasa rayuka, da rufe makarantu, da kaura daga gidaje, da kuma durkushewar harkokin tattalin arziki a wasu yankuna. Wadannan matsaloli suka sa Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu ya ayyana dokar ta-ɓaci kan matsalar tsaro, domi...
Show more...
1 week ago
18 minutes

Najeriya a Yau
Yadda Kiristoci Ke Gudanar Da Bikin Kirsimeti A Cikin Musulmi
Send us a text A duk faɗin Arewacin Najeriya, ana gudanar da bukukuwan Kirsimeti cikin kwanciyar hankali da fahimtar juna, duk da kasancewar Musulmai ne suka fi rinjaye a yawancin yankuna. Kiristoci kan yi bukukuwansu cikin mutunta al’adar Musulmai, yayin da Musulmai kuma ke nuna goyon baya ta hanyar gaisuwa, da tsaro, da mu’amala ta zamantakewa. A wurare da dama kamar Kaduna, Jos, Zaria, Minna da wasu sassan jihar Kano, ana ganin Kiristoci suna zuwa coci ba tare da tsangwama ba, yara s...
Show more...
1 week ago
16 minutes

Najeriya a Yau
'Halin Kunci Da Muke Ciki A Sansanin Gudun Hijira Yayin Bikin Kirsimeti'
Send us a text A yayin da al’ummar Kirista a sassa daban-daban na ƙasar nan ke gudanar da bukukuwan Kirsimeti cikin walwala, da annashuwa da haɗuwa da iyalai, akwai kuma waɗanda wannan lokaci ya zo musu cikin ƙunci da jimami. Waɗannan su ne mutanen da matsalolin tsaro—kamar hare-hare da rikice-rikice—suka tilasta musu barin gidajensu da muhallansu. A maimakon shagulgula a cikin gidajensu, suna gudanar da bikin ne a sansanonin gudun hijira, inda rayuwa ta cika da ƙalubale, da rashin is...
Show more...
1 week ago
14 minutes

Najeriya a Yau
Yadda Farashin Kayayyaki Suke Gabanin Bukukuwan Kirsimeti
Send us a text Gabannin bukukuwan Kirsimeti, kasuwanni a sassan ƙasar nan sun cika sun bunkasa. Jama’a na ci gaba da zirga-zirga domin sayen kayan bukukuwa, yayin da ‘yan kasuwa ke kokarin jawo hankalin masu saye ta hanyar daidaita farashi. A wannan shekarar, alamu sun nuna ba a samu hauhawar farashin kayayyaki a yawancin kasuwanni ba, sai dai wasu na kokawa da rashin kudaden saye. Ko yaya hakikanin farashin kayayyakin suke a wasu kasuwannin Nnajeriya? Wannan shine batun da sh...
Show more...
1 week ago
14 minutes

Najeriya a Yau
Cushe-cushen Da Ake Zargin An Yi A Sabbin Dokokin Haraji
Send us a text Takaddama mai zafi ta dabaibaye sabbin dokokin haraji da Majalisar Tarayya ta amince da su, bayan zarge-zargen cewa an samu sauye-sauye a cikin dokokin bayan an kammala dukkan matakan amincewa da su a majalisa. Batun da ya taso ya jawo cece-kuce daga ‘yan majalisa, jam’iyyun adawa da kungiyoyin fararen hula, inda suke tambayar sahihancin abin da aka mika wa Fadar Shugaban Kasa domin aiwatarwa. Masu suka na cewa sauye-sauyen da ake zargin an yi ba tare da amincewar majalisa ba...
Show more...
2 weeks ago
19 minutes

Najeriya a Yau
Irin Asarar Da Aka Tafka A Kasuwar Kafintoci Dake Kano
Send us a text Gobara a irin wannan yanayi na iska musamman a kasuwanni da gidaje ba sabon abu bane kuma ba abun mamaki ba. Wasu kafintoci dake aiki a kasuwar lale dake unguwar Tal’udu a karamar hukumar Gwale dake jihar Kano sun wayi gari da alhinin gobarar da ta yi sanadiyyar raba su da hanyar abincinsu. Wannan gobara da ba’a san musabbabinta ba ta janyo asarar miliyoyin Naira tare da jefa wadanda abun ya shafa cikin mawuyacin hali. Ko wanne irin hasara aka yi a wannan gobara? Wannan...
Show more...
2 weeks ago
18 minutes

Najeriya a Yau
Darasin Da Za a Yi Koyi Dashi Cikin Takaddamar Dangote Da Farukh Ahmed
Send us a text Murabus din da Shugaban Hukumar Kula da Harkokin Mai ta kasa Ahmed Farukh ya yi daga mukaminsa ya sa ‘yan Najeriya da dama na ta tofa albarkacin bakinsu musamman a bangaren harkokin mai. Murabus din na zuwa ne bayan doguwar takaddama tsakaninsa da Shugaban Rukunin Kamfanin Dangote, Alhaji Aliko Dangote kan batutuwa da dama. Shin ko wanne darasi za a koya daga wannan takaddama da ta kai ga murabus din shugaban. Wannan shine batun da shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai y...
Show more...
2 weeks ago
18 minutes

Najeriya a Yau
Yadda Takunkumin Amurka Zai Shafi Tattalin Arzikin ‘Yan Najeriya
Send us a text Takunkumin da Shugaban Ƙasar Amurka, Donald Trump, ya sanya wa wasu ‘yan Najeriya ya sake jawo hankali kan irin tasirin manufofin ƙasashen waje ga rayuwar mutane da tattalin arzikin ƙasa baki ɗaya. Wannan takunkumi, wanda ya haɗa da hana shiga Amurka, da toshe kadarori ko hana mu’amala da wasu hukumomi da kamfanonin Amurka, ba wai hukunci ne ga mutum ɗaya kaɗai ba, kazalika yana da tasiri mai zurfi ga harkokin kasuwanci, zuba jari da martabar ƙasa a idon duniya. Ko ta y...
Show more...
2 weeks ago
16 minutes

Najeriya a Yau
Ce-ce Ku-ce Da Ya Dabaibaye Dauke Shalkwatar Bankin Masana’antu Zuwa Legas
Send us a text Batun matakin da gwamnatin tarayya ta dauka na mayar da shalkwatar Bankin Masana’antu zuwa jihar Legas ya haifar da ce-ce-ku-ce a tsakanin ’yan Najeriya. Wannan mataki ya tayar da mabanbantan ra’ayoyi daga bangarori daban-daban na al’umma, inda wasu ke kallonsa a matsayin shawara mai ma’ana da za ta karfafa harkokin masana’antu da jawo jarin cikin gida da na kasashen waje. Sai dai a daya bangaren kuma, akwai masu sukar wannan mataki, inda suma suka bayyana irin tasu damuwa ka...
Show more...
3 weeks ago
14 minutes

Najeriya a Yau
Yadda Matsalar Tsaro Ke Hana Mu Tafiye-tafiyen Kirsimeti
Send us a text A ’yan shekarun nan, lokaci na bukukuwan ƙarshen shekara—wanda a da ake ɗauka a matsayin lokacin farin ciki, da haɗuwa da iyalai, da tafiye-tafiye—ya fara sauya salo ga mutane da dama. Maimakon shirye-shiryen ziyartar ’yan uwa ko halartar bukukuwa a garuruwa daban-daban, mutane da yawa yanzu suna cike da fargaba da damuwa. Babban dalilin hakan shi ne ƙalubalen tsaro da ke ƙara tsananta a sassa daban-daban. Rahotanni na hare-haren ’yan bindiga, da sace-sace a kan manyan hanyoy...
Show more...
3 weeks ago
15 minutes

Najeriya a Yau
Alfanu Da Kalubalen Sabon Jadawalin Karatun Makarantu Da Gwamnati Ta Bijiro Dashi
Send us a text A kwanakin baya, Gwamnatin Tarayya ta kaddamar da sabon tsarin jadawalin karatu ga makarantun firamare da sakandare. Sabon tsarin, wanda Ma’aikatar Ilimi ta ƙasa ta tsara, yana da nufin inganta koyarwa da koyo, da rage nauyin lodi ga dalibai, da kuma tabbatar da cewa malamai suna da isasshen lokaci don isar da darussa tare da kwarewa. Tsarin ya mayar da hankali kan daidaita ranakun makaranta, da tsara lokutan darussa bisa bukatun shekaru da matakin karatu, da kuma kara aiki a ...
Show more...
3 weeks ago
15 minutes

Najeriya a Yau
Yadda Abincin Da Mutane Ke Ci Ke Zamewa Guba
Send us a text A yau al’ummar mu na fuskantar barazana ta wata siga da ba kasafai ake gane ta ba, wato guba da ke shiga jikin ɗan Adam ta hanyar abinci irin su nama, kifi, madara da sauran kayayyakin da muke ci a kullum. Sau da yawa dabbobi ko kifaye suna cin wasu tsirrai, ganye, ko ababen da ke dauke da sinadarai masu haɗari, waɗanda daga baya suke taruwa a jikinsu har su zama guba ga mutum idan aka ci su. Wasu lokuta ma waɗannan gubobi ba daga abincin dabbar suke fitowa ba, sai dai daga s...
Show more...
4 weeks ago
17 minutes

Najeriya a Yau
Kudaden Da Samar Da ‘Yansandan Jihohi Zai Lashe
Send us a text Batun samar da ‘yansandan jihohi na ƙara ɗaukar hankalin ‘yan Najeriya, musamman a dai-dai lokacin da matsalar tsaro ke ƙara ta’azzara a sassa daban-daban na ƙasar nan. Sai dai, samar da ‘yansandan jihohi ba abu ne mai sauƙi Kamar yadda wasu ke tunani ba. Gwamnatocin jihohi na buƙatar abubuwa masu yawa kafin su iya ɗaukar wannan nauyi, banda batun samar da dokar samar da wadannan ‘yansanda, akwai batun samar da kayan aiki da horo da sauran abubuwa da ake bukata don gudan...
Show more...
4 weeks ago
22 minutes

Najeriya a Yau
Abun Da Masu Ruwa Da Tsaki Ke Yi Na Dakile Laifuka A Wurin Matasa
Send us a text Masu iya magana kan ce banza ba ta kai zomo kasuwa. In ba haka ba, me ya kai matasan da ake zargi da aikata manyan laifuffuka ofishin ’yan sanda, suka kuma fit oba tare da wani ya harae su ko ya yi mutsu tsawa ba, balle ya saka su a cell? ’Yan sandan dai sun ce wannan wata dabara ce ta yakar aikata manyan laifuka irin su sata da fashi da makami da kwacen waya da fyade kai har ma da satar mutane don kudin fansa a tsakanin matasa. Ko yaya wannan dabara take aiki? Wannan s...
Show more...
1 month ago
24 minutes

Najeriya a Yau
Matsalar Kansar Mama Da Hanyoyin Magance Ta
Send us a text Cutar kansar mama na ɗaya daga cikin manyan cututtukan da ke addabar mata a Najeriya da ma duniya baki ɗaya. An kiyasta cewa mata sama da dubu ɗari biyu na kamuwa da cutar a kowace shekara a Najeriya, yayin da miliyoyin mata a duniya ke fama da wannan cuta. Abin damuwa shi ne cewa yawancin lokuta ana gano cutar ne a kurarren lokaci, wanda hakan ke sa magani ya yi wahala kuma ya rage yiwuwar ceto rayuwar wanda ya kamu da shi. Wannan shine batun da shirin Najeriya A Yau...
Show more...
1 month ago
28 minutes

Najeriya a Yau
Halayen Da Ambasadoji Ya Kamata Su Mallaka Kafin Tura Su Wasu Kasashe
Send us a text A mafi yawan ƙasashen duniya, ana ɗaukar jakadu a matsayin fuskar ƙasa kuma ginshiƙan hulɗar diflomasiyya. Saboda haka, akwai muhimman halaye da suke tilas jakadan ƙwarai ya mallaka domin ya wakilci ƙasarsa cikin mutunci, da nagarta da kwarewa. Tun bayan da shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya fitar da sunayen jakadu da yake sa ran majalisar kasa ta tantance ne dai batun ke ta shan suka daga manazarta kan sunayen da ya fitar. Ko wadanne irin halaye ya kamata jakada ya m...
Show more...
1 month ago
24 minutes

Najeriya a Yau
Waiwaye Kan Irin Gudunmawar Da Sheikh Dahiru Bauci Ya Bayar Ga Cigaban Addini
Send us a text Sheikh Dahiru Usman Bauchi, fitaccen malamin addinin Musulunci, masanin tafsiri, kuma jagoran darikar Tijjaniyya, shahararre ne saboda iliminsa mai zurfi da tasirin da ya yi a fagen addini da tarbiyya a Najeriya da ma ƙasashen Yammacin Afirka. Sheikh Dahiru Bauci ya shafe sama da shekaru saba’in yana koyar da ilimi, ya gudanar da tarukan tafsiri a duk shekara, ya gina makarantu, ya kafa cibiyoyi, kuma ya ba da ilimi ga dubban almajirai hanyoyin da suka taimaka wajen yaɗa ...
Show more...
1 month ago
24 minutes

Najeriya a Yau
Send us a text A fagen siyasar Najeriya a halin yanzu, ana ta ce-ce-ku-ce kan wacce ce babbar jam’iyyar adawa da za ta iya tsayawa ƙafada da ƙafada da jam’iyyar APC mai mulki. Wannan takaddama ta fi karkata ne tsakanin jam’iyyar PDP, wacce ta dade tana taka rawa a matsayin babbar jam’iyyar adawa bayan ficewarta daga mulki a 2015, da kuma jam’iyyar ADC, wacce a ‘yan shekarun nan ta fara samun karɓuwa sakamakon shigar wasu manyan ‘yan siyasa da kuma ƙoƙarin gina sabuwar haɗaka a matsayin madadi...